
Matashiyar nan da ta lashe gasar sarauniyar kyau da masana'antar Nollywood ta shirya za ta fara aikin toshe ramuka da ke titunan Najeriya.
Miss Ozohu-Salihu za ta gudanar da ayyukan tushe ramukan ne a jihohin Najeriya 36.
Matashiyar mai suna Ozohu-Salihu ta furta haka ne jiya Litini yayin da ta ke zantawa da yan jarida a birnin Lokoja da ke jihar Kogi, arewa maso tsakiyar Najeriya.
Ozohu-Salihu ta ce aikin na daya daga cikin ayyukan da zai faranta mata rai domin aiki ne na ceton rayukan al-umma a kasar.
Miss Salihu ta ce, ta damu da afkuwar hadura a kan titunan kasar, haka ne ya sa ta yanke shawarar yin wannan aikin.
Ta ce, hakan zai taimaka matuka wajen rage asarar rayuka da ake samu a kowace rana a fadin Najeriya.