• 18 Jun, 2025

'Yan Bindiga Sun Kwashe Mutum 150 A Gobir

'Yan Bindiga Sun Kwashe Mutum 150 A Gobir

bandits-1-705x400.jpg

Sama da mutum 150 ne akayi garkuwa da su a wani sabon hari da 'yan bindiga suka kai kauyukan Gobir da ke jihar Sokoto arewa maso yammacin Najeriya.

'Yan bindigan sun kuma sace shanu sama da guda 1000 yayin hare-haren da suka kaddamar kan al'ummar yankunan.

'Yan ta'addan sun kai hare-haren ne kwanaki kadan bayan kashe sarkin na Gobir Alhaji Isa Muhammad Bawa bayan sunyi garkuwa da shi.

Farfesa Bello Bada na tsangayar koyon harshen Turanci a jami'ar Usman Danfodiyo da ke Sakkwato ya tabbatar da hare-haren, inda ya ce abin takaici ne   dawowar 'yan bindigan kwanaki kadan bayan sun hallaka sarkin Gobir.

Farfeasa Bello ya kara da cewa akwai zarge-zargen cewa wasu mutane daga cikin al'ummar Gobir da kewaye na da hannu a cikin ta'addancin da ke faruwa, domin suna zance da 'yan bindigan ta wayar salula.

Ahmed Abubakar

How puzzling all these changes are! I'm never sure what I'm going to turn into a tidy little room.