
Yan bindiga sun hallaka wani babban jami'in kula da fasa kwauri a yankin Koko dake jihar Kebbi, arewa maso yammacin Najeriya.
Yan bindigan a lokaci guda sunyi garkuwa da wani jami'in a wani hari da yan bindigan suka kai yayin da jami'an ke ziga-zirgar aiki.
Mai magana da yawun hukumar ta fasa kwauri shiyyar jihar ta Kebbi Mohammed Tajuddeen Salisu ne ya bayyana hakan a birnin Kebbi.
Tajuddeen ya kara da cewa yan bindiga sun bukaci kudin fansa bayan sun kama jami'in nasu yayin da suka kaske Dabo Umar.
Tajuddeen yace, a yanzu haka babban jami'in Babagana Abba Kabiru yana hannun yan bindigan.
Muhammed Tajuddeen yace sun kai gawar jami'in nasu Dabo Umar da yan bindigan suka kashe Kaduna domin binne shi.