
Wani mutum mai shekaru 58 ya mutu bayan ya shafe kwanaki goma sha tara yana azumi.
An samu gawar mutumin ne a yankin Alagbado da ke birnin Legas kudu maso yammacin Najeriya.
Mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar Lagas Benjamin Hundeyin ne ya furta haka a birnin na Eko.
Rahotanni sun tabbatar da mutuwar ta shi misalin karfe 6 na safiyar jiya Talata.
Hundeyin ya ce, dan uwan mamacin wanda shi ma ba a bayyana sunan shi ba shi ne ya sanar da yan sandan yankin Alagbado lamarin.