
Gwamnan jihar Taraba Agbu Kefas ya marabci tsohon shugaban kasar Najeriya Goodluck Ebele Jonathan.
Kefas ya marabci Goodluck Jonathan ne a filin tashi da saukar jiragen sama na Danbaba Suntai da ke babban birnin jihar Jalingo.
Gwamnan jihar Kogi Usman Ododo na d cikin tawagar Gwamna Agbu Kefas a filin jirgin domin tarbar tsohon shugaban kasar.
Tuni gwamnonin PDP da sauran masu ruwa-da-tsaki a jam'iyyar suka taru a jihar ta Taraba domin tattauna matsalolin jam'iyyar wadanda suka hada da matsalar jihar Rivers da sauransu.
Ana rade-radin cewar hankalin yan jam'iyyar ta PDP ya fara karkata kan yiwuwar dawo da tsohon shugaban kasar Jonathan domin yin takarar neman mulkin kasar karo na biyu a shekarar zabe ta 2027.