• 18 Jun, 2025

Sojoji Da Yan Sanda Sun Kaiwa Masu Zanga-Zangar Lumana Hari A Abuja

Sojoji Da Yan Sanda Sun Kaiwa Masu Zanga-Zangar Lumana Hari A Abuja

screenshot-20240805-130846-1722860000730.jpg

Jami'an tsaro a Najeriya sun fara aikin hadin gwiwa tsakanin sojoji da yan sandan kasar domin tarwatsa masu zanga-zanga a babban birnin kasar Abuja.

An ga yan sanda na harba barkonon tsohuwa kan masu zanga-zanga wadanda suka hallara a rana ta biyar domin nuna rashin amincewar su da yadda abubuwa ke gudana a kasar.

Yan Najeriya dai sun dage da nuna rashin jin dadin su kan yadda talakawan kasar ke fama da wahalan yunwa da talauci sakamakon cire tallafin mai da rashin darajar kudi a Najeriya.

Rahotanni sun nuna cewa rigimar tsakanin yan kasar da jami'an tsaro ta shafi masu shigewa a kan titi da masu shaguna a birnin, inda suke tserewa don gujewa barkonon tsohuwa.

Jami'an tsaron DSS sun kama shugaban wata kungiyar kare hakkin bil'adama mai suna Adaramoye Michael Lenin a yau litini yayin zanga-zangar.

An ga sojoji da dama a yau fiye da kwanaki hudu da suka gabata a cikin birnin tarayyar Abuja suna kokarin dakile zanga-zangar ta hanyar cin zarafin al'ummar kasar.

 

Ahmed Abubakar

How puzzling all these changes are! I'm never sure what I'm going to turn into a tidy little room.