
Tsohon shugaban tsagerun Naija Delta Asari Dokubo ya zargi shugaban kasa Bola Tinubu da amfani da ministan Abuja Nyesom Wike wajen kawo rikicin siyasa a jihar Rivers.
Idan ba a manta ba Jihar Rivers na cikin rikicin siyasa wanda tsohon gwamnan jihar Nyesom Wike da Gwamna mai ci Fubara ke rigima.
Dokubo Asari ya furta haka ne a cikin wani shiri a tashar talabiji na Arise a yau Talata.
Asari Dokubo ya ce idan Tinubu da Wike suka kuskura suka cire Sim Fubara a kan kujerar mulkin jihar Rivers, tabbas wani abu zai faru.
Asari Dokubo ya yi Allah wadai da halin shugaban kasa Bola Tinubu kan tashin hankalin siyasa da ya haddasa a jihar ta Rivers.
Asari ya ce, a matsayinshi na mai fada aji a jihar, dole ne ya yi tsokaci kan jefa yan jihar Rivers cikin rigingimu da Tinubu ya ke yi ta hanyar amfani da tsohon gwamnan Nyesom Wike.