
Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya sauka a filin tashi da saukan jiragen saman kasa-da-kasa na birnin Riyadh da ke kasar Saudi-Arabia.
Shugaba Tinubu ya tafi kasar Saudin ne domin halartar taro kasa-da-kasa na kungiyar kasashen Musulmai na duniya.
Najeriya dai ta zama daya daga cikin kasashen kungiyar ne bayan ta yi rigista a lokacin mulkin tsohon shugaban sojan kasar Janar Ibrahim Badamasi Babangida.
Ana gudanarda taron ne na kasa-da-kasa tsakanin kasashen Musulmai na duniya domin tattauna matsalolin da ke addabar kasashen na Musulmai a fadin duniya.
Kamar sauran tarurrukan duniya, ana gudanarda taron kungiyar kasashen Musulmai ne a kowani shekara.