• 17 Jun, 2025

Shin Ministan Abuja Nyesom Wike Na Tsoro Ne?

Shin Ministan Abuja Nyesom Wike Na Tsoro Ne?

Shin Ministan Abuja Nyesom Wike Na Tsoro Ne?

screenshot-20240726-094545-1721983583917.jpg

Ministan babban birnin tarayya Abuja Nyesom Wike ya gargadi masu zanga-zanga da su nesanci birnin tarayya.

Wike ya bayyana wa manema labarai haka ne bayan ganawa da jami'an tsaro a Abuja a jiya Alhamis.

Ministan ya ce, duk da cewa 'yan Najeriya sunada 'yancin gudanar da zanga-zanga lumana, amma ba a birnin tarayya ba.

Ministan dai ya buya da ayyana ranar 1 ga watan Agusta ta zama ranar gudanar da bikin karrama sarakunan gargajiyan yankin birnin na tarayya don kassara zanga-zangar.

Yayin da ya kai ziyarar bude wani aikin a yankin Saburi a Kubuwa dake birnin tarayyar, Wike ya ja hankalin mutane da su kauracewa zanga-zangar 'yan fashi da makami.

Ya ce, zanga-zangar da aka shirya aikin hannun bata gari ne, ba masu kishi ko son kasar ba, don haka, jama'a suyi hankali.

Ahmed Abubakar

How puzzling all these changes are! I'm never sure what I'm going to turn into a tidy little room.