• 17 Jun, 2025

Shin gwamnatin Tinubu ba ta jure wa suka ne?

Shin gwamnatin Tinubu ba ta jure wa suka ne?

Shin gwamnatin Tinubu ba ta jure wa suka ne?

0d859960-4470-11ef-b74c-bb483a802c97png.webp

A yanzu haka dai akwai alamun rashin jituwa da kuma zaman ƴan marina a tsakanin waɗansu ƴan majalisar dattijan Najeriya sakamakon cire mai tsawatarwa na majalisar, Sanata Muhammad Ali Ndume.

Bayanai sun nuna cewa Sanatoci daga arewacin Najeriya sun soma wani yunkuri na haɗa kansu waje guda ganin cewa duk wanda ya soki gwamnatin Tinubu ana sa kafa a shure shi.

A baya ma an dakatar da Sanata Abdul Ningi daga zauren majalisar sakamakon zargin cewa an yi cushe a kasafin kudin kasar. Zargin da majalisar ta musanta.

Ma’abota shafukan sada zumunta sun yi ta zazzafar mahawara a tsakaninsu sakamakon abin da suka ce majalisar dokokin ƙasar na cikin aljihun ɓangaren zartarwa ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.