
Daruruwan mutane sun fito tituna a birnin Legas a rana ta uku ta zanga-zangar matsin rayuwa da talakan kasar ke ciki a yankin Ojota dake birnin.
Masu zanga-zangar karkashin kungiyar #TakeItBackMovement sunce babu gudu babu ja da baya a kokarin su na neman saukin rayuwa a Najeriya.
Matasan dake dauke da kwalaye suna gudanar da zanga-zangar lumana don samun biyan bukatun su da gobe mai kyau daga gwamnatin Bola Tinubu.
A wani lamari da ya shafi zanga-zangar kuma, yan Najeriya su na ci gaba da nuna damuwar su kan yadda mahukunta suke hana masu zanga-zangar fita tituna a sassan kasar dake da jihohi 36.
Duk da haka, yan kasar sun ci gaba da anniyar su ta zagaya titunan biranen kasar domin gudanar da zanga-zangar cikin yanci da walwala.