
Hukumar kula da girgizar kasa ta Najeriya ta ce tsagewar kasa da ta faru a birnin tarayya Abuja ba mai karfi ba ne.
Shugaban hukumar Farfesa Olusegun Ige ne ya furta hakan yau Laraba inda ya ce hukumar su ta sa idanu a kan lamarin kuma babu wata illa sosai.
Farfesa Ige ya kara da cewa babu wata alama ko hujjar cewa tsegewar kasar za ta iya zama babban barazana ga mazauna birnin.
Farfesa Ige ya ce sagewar kasar da ta faru a yankin Katampe da ke Abuja ta girgiza kasa sosai cikin kwanaki 5 da su ka gabata.
Farfesan ya kara da cewa girgizar bai wuta tsawon kilomita biyar ba daga dakin tattara bayanai, inda su ka je wajen domin ganin abinda ya fara.