• 18 Jun, 2025

Dan Takarar Shugaban Kasa A Jam'iyyar APC Ya Bawa Tinubu Shawara

Dan Takarar Shugaban Kasa A Jam'iyyar APC Ya Bawa Tinubu Shawara

Dan Takarar Shugaban Kasa A Jam'iyyar APC Ya Bawa Tinubu Shawara

olawepo-hashim.jpg

Tsohon dan takarar shugaban kasa a jam'iyya mai mulki ta APC Gbenga Hashim ya shawarci shugaba Bola Tinubu da ya warware matsalolin da za su jefa kasar cikin zanga-zanga.

Hashim yace abu ne mai sauki idan shugaban kasa ya saurari bukatun yan kasa da zummar warware su domin kaucewa shiga zanga-zangar da za'a fara ranar 1 ga watan Agusta mai kamawa.

Hashim yace haka ne kadai mafita domin ba'a san abin da zanga-zangar za ta haifar wa Najeriya ba idan tayi tasira har zuwa kwanaki goma ko fiye da haka.

Tsohon dan takaran shugaban kasan ya kuma gardadi masu niyyar zanga-zangar da suyi taka-tsan-tsan don kaucewa amfani da hanyar da ba ta dace ba wajen illata zababbiyar gwamnati.

Gbenga Hashim yace, duk da cewa yan kasa na da yancin gudanar da zanga-zanga kamar yadda tsarin mulkin kasa ya tanadar, akwai tsoron kada wasu su buya a bayan zanga-zangar su aikata abin da bai kamata ba.

Hashim yace, don haka, akwai bukatar gudanar da zanga-zanga cikin lumana kamar yadda kundin tsarin mulkin Najeriya da ma dimukradiyya suka shimfida.

 

 

 

 

 

 

 

Ahmed Abubakar

How puzzling all these changes are! I'm never sure what I'm going to turn into a tidy little room.