• 17 Jun, 2025

Boko Haram Sun Kashe Sojojin Najeriya A Borno

Boko Haram Sun Kashe Sojojin Najeriya A Borno

Boko Haram Sun Kashe Sojojin Najeriya A Borno

gettyimages-1248029000-612x612-1.jpg


A kalla sojoji 7 sun hallaka sakamakon wata nakiya da ta tashi a jihar Borno, arewa maso gabashin Najeriya.

Lamarin ya faru ne bayan rundunar sojan Najeriya ta aika sojoji tarwatsa 'yan kungiyar Boko Haram da suka kai hari a wata kauye a jihar ta Borno.

Rahotanni sun tabbatar da cewa motar sojan Najeriya ta taka wata nakiya da aka dasa kan tirin Gamboru-Ngala, inda ta amsa ta hallaka sojojin guda 7 a cikin motar su.

Rahotannin sun bayyana cewa soji guda daya ne cikin sojoji 8 dake cikin motar sojojin ya rayu bayan tashin nakiyar.

Motoci da dama dake kan titin yayin da nakiyar ta tashin sun lalace. An ruwaito sojojin Najeriya na ta fadi-tashi don tattara gawakin 'yan'uwansu da suka rigamu gidan gaskiya a iftila'in.

A cewar rundunar sojin Najeriya, motocin soja guda uku aka aikawa kauyen domin ceto al'ummar. Mota ta farko da ta biyu sun shige, amma ta karshe ce ta hau kan nakiyar.

 

Ahmed Abubakar

How puzzling all these changes are! I'm never sure what I'm going to turn into a tidy little room.