• 17 Jun, 2025

An Kafa Dokar Hana Fita A Jihohin Kano Da Borno Da Yobe

An Kafa Dokar Hana Fita A Jihohin Kano Da Borno Da Yobe

screenshot-20240802-081921-1722583203044-1722583238581.jpg

Gwamnatin jihar Kano ta kafa dokar hana fita a fadin jihar sakamakon tashin hankali da zanga-zangar lumana ya zama.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ne ya furta hakan yayin taron manema labarai a gidan gwamnatin jihar Kano a jiya Alhamis.

Gwamnan yace dokar hana fitan ta zama wajibi duba da yadda zanga-zangar da aka  shirya na lumana ta rikide zuwa sace-sacen dukiyar gwamnati da na al'umma.

Abba Kabir Yusuf yace, matasa sun buge da kone-kone da sace-sacen kayayyakin da ba mallakin su ba wanda hakan ya tilasta aka samu asarar rayuka a zanga-zangar.

Gwamnan ya umarci jami'an tsaro a jihar ta Kano su tabbata dokar hana fita ta yi tasiri a fadin jihar domin dawoda zaman lafiya da doka da oda.

A jihar Yobe, Gwamnatin jihar ta kafa dokar hana fita a karuruwan Gashuwa da Potiskum da Nguru na tsawon awanni 24 sakamakon sace-sace da wasu matasa suka aikata.

Mai bawa Gwamna shawara kan harkokin tsaro Dahiru Abdussalam ne ya bayyana haka a cikin wata takarda da aka rabawa manema labarai.

Wani lamari dake da alaka da tashin hankali a jihar Borno shima ya tilasta gwamnatin jihar ta Borno kafa dokar hana fita a karamar hukumar Konduga, bayan yan kungiyar Boko Haram sun kai hari kauyen Kauri suka hallaka mutum 16.

Ahmed Abubakar

How puzzling all these changes are! I'm never sure what I'm going to turn into a tidy little room.