
Masu zanga-zanga a Najeriya sun fito titunan babban birnin kasar Abuja a kokarin su na neman saukin rayuwa ga mahukuntan kasar.
Yau Juma'a rana ce ta biyu ta zanga-zangar da aka fara jiya Alhamis a fadin kasar sakamakon halin kunci da talakan kasar ke ciki.
Masu zanga-zangar dai sunce sun kosa da mulkin danniya da ake gudanar wa a Najeriya tun dawowar kasar tafarkin dimukradiyya a shekarar 199.
Yan kasar sun bayyana yadda abubuwa suka tabarbare a Najeriya duk da dumbun arzikin da Allah ya yi wa kasar dake yankin Afrika ta yamma.
Jami'an tsaro dai sun yi kokarin dakatar da mutane yin zanga-zangar musamman jiya Alhamis amma hakan bai yiwu ba.